WA'adi na na ukku:An soma yakin neman zaben Ivory Coast.

 An soma yaÆ™in neman zaÉ“e a Ivory Coast

A yau Laraba ake soma yaƙin neman zaɓe a Ivory Coast gabannin zaɓen shugaban ƙasar da za a yi a karshen wannan wata.

Jam’iyyun adawa na ci gaba da yin kira ga jama'a su amsa kiran fitowa zanga zanga, don daÆ™ile aniyar shugaba mai ci Alassane Ouattara ta yin tazarce a karo na uku.

Dubban mutane sun yi zanga-zangar adawa da wannan matakin a babban birnin kasuwanci na Abidjan, a ranar Asabar.

An hana Æ´an takara hudu na manyan jam'iyyun adawa shiga zaben.

Mista Ouattara ya zama shugaban Ivory Coast me shekaru goma da suka gabata, yayin wani zaɓe mai cike da kace-nace.


Post a Comment

Your comment will be directly sent to the website developer.

Previous Post Next Post