Mutane sun gudanar da saukar Alqur'ani da kuma addu'o'i a jahar Borno kan rashin tsaro da jahar ta ke fama da shi.



Mutanen Borno sun yi addu’oi sama da miliyan 41

a jihar Borno da ke arewa maso gabashin Najeriya

domin neman kawo ƙarshen masifar da mayakan

kungiyar Boko Haram suka jefa su a ciki.

Wata ƙungiya ce mai suna Borno Concerned Citizen

wato Æ´an jihar da suka damu da halin da take ciki

ta jagoranci taron addu’o’in a ranar Lahadi.

Barista Zahra Maiduguri É—aya daga cikin waÉ—anda

suka jagoranci addu’o’in ta ce an yi saukar Al

Æ™ur’ani da kuma addu’oi 41, 837,016 domin neman

sauƙin masifar da jihar take ciki.

Daga cikin addu’o’in har da “Istigifari” miliyan

13,669,000 da “Ya LaÉ—ifu” miliyan 10,688,00.

An kuma yi “Ya Kahharu” fiye da miliyan É—aya da

salatin Annabi da kuma salatil fati.

Baya ga addu’u’oin an kuma yanka dabbobin shanu

da nufin yin sadaka domin Allah ya biya buƙata.

Ƙungiyar ta kunshi shugabanni na siyasa da na

gargajiya da malaman addini da malaman Boko a

jihar Borno.

Mayakan Boko Haram sun kwashe fiye da shekara

goma suna kai hare-hare a arewacin Najeriya,

musamman a jihohin Borno da Yobe da kuma

Adamawa.

Hare-haren sun yi sanadin mutuwar dubban mutane

da kana suka raba miliyoyin jama'a da gidajensu.

Harin Zabarmari inda ƙungiyar ta yi wa manoma

yankan rago shi ne hari na baya-bayan nan mafi

muni da Boko Haram ta kai a jihar Borno.

Post a Comment

Your comment will be directly sent to the website developer.

Previous Post Next Post