Kin tabbata mai mulkin mallaka:yariman Saudiyya ya fadawa Isra'ila

 


Yariman Saudiyya Turki Al-Faisal ya caccaki

Isra’ila

Yariman Saudiyya Turki Al-Faisal bin Abdulziz al-

Saud, kuma tsohon shugaban hukumar leƙen asirin

Æ™asar ya caccaki Isra’ila inda ya kira ta babbar mai

mulkin mallaka da ke amfani da ƙarfi da rusa

matsugunin FalasÉ—inawa.

Yarima Turki al Faisal ya yi waÉ—annan kalaman ne a

wani taron tsaro ta intanet da Bahrain ke jagoranta

a Manama a ranar Lahadi wanda ya samu halartar

ministan harakokin wajen Isra’ila Gabi Ashkenazi

wanda ya yi watsi da kalaman.

Al-Faisal ya Æ™ara da cewa “Isra’ila tana rusa gidaje

yadda ta ga dama kuma tana kashe duk wanda

take so.”

Amma a martaninsa, ministan harakokin wajen

Isra’ila ya ce ya tausayawa kalaman da suka fito

daga yariman.

Ya wallafa a shafinsa na Twitter cewa “zargin karya

da jami’in Saudiyya ya yi a taron Manama ba ya

nuna gaskiya ko asalin canjin da yankin ke ciki."

View more on Twitter

Zafafan kalaman da suka fito daga Yarima Turki al

Faisal a wajen taron Manama ya nuna girman

ƙalubalen duk wata yarjejeniya da ake son cimma

tsakanin Æ™asashen Larabawa da Isra’ila muddin

babu batun cin gashin kan Faladinawa.

Kuma wannan na faruwa ne a yayin da manyan

ƙasashen Larabawa kamar Bahrain da Daular

Larabawa suka yi maraba da Isra’ila a wajen taron

bayan daidaita hulÉ—arsu da Isra’ila da gwamnatin

Trump ta jagoranta.

Post a Comment

Your comment will be directly sent to the website developer.

Previous Post Next Post